Jirgin saman kasar Turkiya ya yi hadari a Kirgistan
January 16, 2017Talla
Bayan dai wani adadi na farko da ya sanar da mutuwar mutane 15, zuwa 20 a ofishin ministan kiwon lafiya na kasar ta Kirgistan ya sanar da wannan sabon adadi na mutane 32 cikinsu har da matukan jirgin guda hudu, inda wata majiya ta asibitoci ta tabbatar da kasancewar yara kanana guda shida daga cikin wadand suka mutu.
Jirgin dai ya taso ne daga birnin Hong-Kong na kasar Chaina, kuma ya fadi ne a kusa da filin jirgin saman Manas na jihar Bichkek sakamakon rishin kyawon yanayi a cewar Moukhammed Svarov, wani jami'in ma'aikatar agaji ta kasar Kirgistan.