Jamus na ɗaukar matakai a kan Ebola
August 13, 2014Talla
Ɗaukar wannan mataki ya biyo bayan ƙarin jama'ar da ake samu da ke mutuwa waɗanda suka kamu da cutar ta Ebola a cikin ƙasashen yankin na yammancin Afirka.
Wani kakakin ofishin ministan harkokin waje na ƙasar ta Jamus Martin Schäfer; ya ce kiran bai shafi jami'an kiwon lafiya ba, da masu aiki agaji da ke ba da tallafin gaggawa , sannan ya ce ofishin jakadancin Jamus ɗin zai ci gaba da kasancewa a buɗe a cikin ƙasashen.
Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Umaru Aliyu