1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan gudun hijira sun ga ta kai a teku

Yusuf Bala Nayaya
May 15, 2019

Kungiyar agaji ta Sea-Watch ta kasar Jamus ta bayyana cewa ta ceto bakin haure 65 daga teku bayan sun baro gabar teku daga Libiya a wannan rana ta Laraba,

https://p.dw.com/p/3IZ6w
Migranten vor der libyschen Küste
Hoto: picture-alliance/AP Photo/F. Heinz

Ministan harkokin cikin gidan Italiya me ra'ayin rikau Matteo Salvini ya sha alwashi na cewa ba zai bari ba a kawo 'yan gudun hijirar zuwa gabar teku a Italiya.

An dai kwaso 'yan gudun hijirar a tsakiyar ruwan kasa da kasa da tazarar kilomita 55 arewa daga tashar gabar teku ta Zuwara, kuma a cewar mai magana da yawun kungiyar ta Sea-Watch dukkanin mutanen da aka ceto suna tare da su.
Salvini dai da ke zama mai ra'ayin rikau kan adawa da shigowar bakin ya ce ta hanyar daukar mataki mai tsauri ne kawai zai sa bakin hauren su rika shayin yin kasada ta ratso teku a kokari na kai wa Turai daga Afirka.

Ya dai sha wannan alwashi na nuna adawa da zuwan bakin adaidai lokacin da 'yan takara ke kara zawarcin kuri'un masu zabe, a zaben 'yan majalisar Tarayyar Turai a ranar 26 ga watan nan na Mayu a Italiyan.