1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Isra'ila ta kai hari Lebanon bayan yin sulhu

June 20, 2026

A kalla mutane biyar ne suka mutu a hare-haren ta sama da Isra'ila ta kai kudancin Lebanon, sa'o'i kadan bayan an yi sulhu tsakanin Isra'ilar da kuma mayakan Hezbollah.

https://p.dw.com/p/5FkIA
Isra'ila ta kai hari Lebanon
Hoto: Stringer/REUTERS

Kamfanin dillancin labarai na Lebanon ya ruwaito cewa, Isra'ila ta yi amfani da jiragen yaki da kuma jirage marasa matuka wajen kai farmakin yankin Nabatieh a cikin daren, wanda ya yi sanadin lalacewar rukunin gidajen jama'a.

Karin bayani: Tsagaita wuta tsakanin Isra'ila da Lebanon ta fara aiki

A ranar Juma'a ce Isra'ila da Hezbollah suka amince da yarjejeniyar tsagaita bude wuta biyo bayan wani kazamin fada a Lebanon wanda ya halaka mutane 47, yayin da Isra'ila ta tabbatar da mutuwar sojojinta hudu, lamarin da ya kara janyo tarnaki ga kokarin shugaban Amurka Donald Trump, na cimma sulhu da Iran, domin samar da zaman lafiya a yankin Gabas ta Tsakiya.