1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zanga-zangar neman sauyi a Iraki

Lateefa Mustapha Ja'afar
January 31, 2020

Babban malamin mabiya mazhabar Shi'a na Iraki Ayatollah Ali al-Sistani ya yi tir da matakan amfani da karfi wajen murkushe masu zanga-zangar adawa da salon mulkin kasar.

https://p.dw.com/p/3X605
Proteste gegen Korruption und Missmanagement im Irak
Masu zanga-zanga a Iraki na neman gyara wajen gudanar da mulkiHoto: Reuters/T. Al-Sudani

Masu zanga-zangar dai na neman a sauke gwamnatin da suke zargi da cin hanci. Sun kuma bukaci a kawo karshen katsalandan din da kasashen ketare ke yi a kasarsu, tun bayan da rundunar taron dangi karkashin jagorancin Amirka ta kifar da gwamnatin tsohon shugaban mulkin kama karyar kasar marigayi Saddam Hussein a shekara ta 2003. Rahotanni sun nunar da cewa kimanin mutane 500 ne suka halaka tun bayan fara zanga-zangar ta baya-bayan nan, da ta rikide zuwa tashin hankali a Irakin.