1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Iraki: Jingine aiyukan jakadancin Amirka

Abdoulaye Mamane Amadou
January 1, 2020

Ofishin jakadancin kasar Amirka da ke Iraki ya bayyana sanarwar dakatar da duk wasu harkokin aikinsa har zuwa illa masha Allahu kwana daya bayan masu zanga zanga sun mamaye harabar ma'aikatar

https://p.dw.com/p/3VZQ2
Irak | Gewaltsame Proteste auf dem Geländer der US Botschaft
Hoto: AP/K. Mohammed

Masu zanga-zangar dai sun mamaye harabar ofishin jakadancin kasar ta Amirka ne tare da jefa duwatsu da kokkona wasu muhimman kayayakin kasar da ke ga jikin ma'aikatar ta huldar jakadancin Amirka a Bagadaza, ciki har da Kyamarori masu daukar hoto daga nesa.

Wata sanarwar da ofishin jakadanci kasar Amirka ta fitar ta shawarci ma'aikatan ofishin da su gujewa zuwa ma'aikatar kana kuma ta dakatar da duk wasu alkawulan tattaunawa ko na bayar da visa da ta daukarwa jama'a.

Tuni wasu rahotanni daga birnin Washington ke cewa babban sakataren harkokin wajen kasar Mike Pompeo ya bayyana matakin dage kai ziyarar aiki a kasar Ukraine biyo bayan kai harin ga ofishin jakadancin Amirka a birnin Bagadaza.