1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hatsari na neman rikidewa ga adawa da gwamnati

Usman ShehuMay 15, 2014

A kasar Turkiya kungiyar kwadogo mafi girma ta kira a shiga yajin aiki a fadin kasar, domin nuna gazawar gwamnati bisa kare mahakar ma'adinai

https://p.dw.com/p/1C0Qn
Türkei Soma Grubenunglück Protest Istanbul 14.05.2014
Hoto: picture-alliance/dpa

A yanzu haka dai fatan samun wani da rai a cikin ramin hakar ma'adinai na kara dushewa, daga mahakar gawoyin kwal a garin Soma da ke yammacin kasar ta Turkiya. Akalla mutane 282 suka rasu, bayan gobara da fashewar wasu sinadarai, abinda ya sa wannan ya kasance hatsiri mafi muni a tarihin masana'antun Turkiyan. A jiya dai dubban mutane ne suka yi arangama da 'yan sanda a biranen Ankara da Instanbul, inda suke zargin gwamnanti da kuma ma'aikatun hakar ma'adinan da sakaci.

Mawallafi: Usman Shehu Usman

Edita: Umaru Aliyu