1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taho mu gama a sansanin sojan Burundi

Lateefa Mustapha Ja'afarDecember 11, 2015

Rundunar sojojin Burundi ta ce 12 daga cikin maharan da suka kai hari a sansanonin sojojin kasar uku, a kokarin da suke na sace makamai tare da sakin firsunoni 'yan uwanasu sun sheka barzahu.

https://p.dw.com/p/1HLwI
'Yan bindiga sun kai hari a kan sojojin Burundi
'Yan bindiga sun kai hari a kan sojojin BurundiHoto: Getty Images/AFP/P. Moore

Mazauna birnin Bujumbura sun ji karar bindigogi da kuma ta abubuwa masu fashewa a yayin artabu tsakanin jami'an sojojin kasar da kuma 'yan bindigar da suka kai harin. A wani jawabi da ya yi a gidan radiyon kasar, kakakin rundunar sojojin Kanal Gaspard Baratuza ya bayyana cewa kawo yanzu sun cafke maharan guda 20, kana daga cikinsu akwai wani wanda ya samu raunuka da a yanzu haka yake karbar magani a asibitin sojojin. Baratuza ya kara da cewa akwai wasu sojoji guda biyar da suka samu raunuka a yayin bata kashin.