1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gobara ta hallaka mutane 232 a Brazil

January 27, 2013

Mahukuntan ƙasar Brazil sun ce aƙalla mutane 232 su ka hallaka sakamakon gobarar da ta tashi a wani gidan rawa

https://p.dw.com/p/17SSG
Fire-fighters try to extinguish a fire at Kiss nightclub in the southern city of Santa Maria, 187 miles (301 km) west of the state capital of Porto Alegre, in this picture taken by Agencia RBS, January 27, 2013. At least 200 people were killed in the nightclub fire in southern Brazil on Sunday after a band's pyrotechnics show set the building ablaze, and fleeing patrons were unable to find the emergency exits, local officials said. Bodies were still being removed from the Kiss nightclub in the southern city of Santa Maria, Major Gerson da Rosa Ferreira, who was leading rescue efforts at the scene for the military police, told Reuters. Local officials said 180 people were confirmed dead, and Ferreira said the death toll would rise above 200. He said the victims died of asphyxiation, or from being trampled, and that there were possibly as many as 500 people inside the club when the fire broke out at about 2:30 a.m. REUTERS/Germano Roratto/Agencia RBS (BRAZIL - Tags: DISASTER TPX IMAGES OF THE DAY) NO SALES. NO ARCHIVES. ATTENTION EDITORS - THIS IMAGE WAS PROVIDED BY A THIRD PARTY. FOR EDITORIAL USE ONLY. NOT FOR SALE FOR MARKETING OR ADVERTISING CAMPAIGNS. THIS PICTURE IS DISTRIBUTED EXACTLY AS RECEIVED BY REUTERS, AS A SERVICE TO CLIENTS. BRAZIL OUT. NO COMMERCIAL OR EDITORIAL SALES IN BRAZIL
Hoto: Reuters

Mahukuntan ƙasar Brazil sun ce aƙalla mutane 232 su ka hallaka sakamakon gobarar da ta tashi a wani gidan rawa mai shaƙe da mutane a garin Santa Maria da ke yankin kudancin ƙasar. Akwai wasu mutane 131 da su ka samu raunuka.

Mafi yawan waɗanda abun ya ritsa da su ɗallibai ne, kuma ana kyautata zaton akwai kimanin mutane 2000, lokacin da wutar ta tashi, yayin da ake wasannin wuta, kamar yadda rahotanni su ka bayyana.

Shugaban ƙasar ta Brazil Dilma Rousseff ta katse halartar taron tsakanin ƙasashen Latin Amurka ta Turai da ke gudana a ƙasar Chile, domin zuwa garin na Santa Maria ta gani da idonta yadda ma'aikatan agaji ke ɗaukan mataki.

'Yan uwa da abokan arzikin mutanen da abun ya ritsa da su, sun hallara yayin da ake aikin fito da gawawakin waɗanda su ka hallaka.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Yahouza Sadissou Madobi