Ghana ta kai karar Togo kan takaddamar iyakar Teku
February 20, 2026
Ghana ta shigar da kara a gaban kotunan kasa da kasa domin warware takaddamar kan iyakar Teku da take yi da makwabciyarta Togo, saboda gaza samun daidaito a tsakanin bangarorin biyu bayan shafe shekaru takwas na tattunawa.
A cikin wata sanarwa da fadar mulki ta Accra ta fitar ta ce tun tuni ta sanar da Lomé cewa za a shata iyakar kasashen biyu bisa tsarin da yarjejeniyar dokokin Teku na Majalisar Dinkin Duniya ya tanadar.
Wannan mataki ya biyo bayan matakin shari'a da Ghana ta dauka a baya kan kasar Côte d'Ivoire, wanda kotun kasa da kasa ta yanke hukunci a 2017, lamarin da ke nuna yadda Accra ke neman tabbatar da tsaron iyakokinta na ruwa masu matukar muhimmaci ga tattalin arzikin kasar.
Wadannan yankuna na gabar Teku da Ghana ke takaddama a kan su na da fadin dubunan kilomitoci kana kuma sun kunshi albarkatun danyen mai da kuma muhimman wuraren kamun kifi.