1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bude kasuwar Kirsimeti a Faransa

Yusuf Bala Nayaya
December 14, 2018

A wannan Juma'ar ce za a bude kasuwar Kirsimeti a birnin Strasbourg na Faransa, kwana guda bayan gumurzu na musayar wuta da dan bindigar da ya kai hari a kasuwar.

https://p.dw.com/p/3A5T1
Straßburger Münster
Hoto: AFP/Getty Images

A ranar Alhamis ce dai minisatan harkokin cikin gidan Faransa Christophe Castaner ya ce tun daga misalin karfe goma sha daya agogon na Faransa wato goma agogon GMT za a tsammaci sake bude kasuwar.

Dan bundugar da ya kai hari a wannan kasuwa a ranar Talata da ta gabata wato Cherif Chekatt, ya bakunci lahira bayan musayar wuta da aka yi tsakaninsa da jami'an tsaro na kasar ta Faransa a ranar Alhamis.

Shi dai maharin dan shekaru 29 wanda dama jami'an tsaro sun san shi da aikata manyan laifuka, sai dai babu na ta'addanci ya bude wuta a kasuwar ta Kirsimeti inda ya halaka mutane uku da wani da wani cikin mawuyacin hali.

Masu gabatar da kara a Faransar dai na duba harin na Talata a matsayin aikin ta'addanci wanda tuni kungiyar IS ke ikirari na da masaniya kansa.