1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Falasɗinu za ta kafa tutarta a Majalisar Ɗinikin Duniya

Abdourahamane HassaneSeptember 10, 2015

Ƙasar za ta kafa tutarta ne a cibiyar Majalisar Ɗinkin Duniya a wani sabon yunƙurin diplomasiyya domin ganin ƙasar ta samu yanci kai.

https://p.dw.com/p/1GU00
Symbolbild Palästina Israel Flaggen Konflikt
Hoto: picture-alliance/dpa

Majalisar Ɗinkin Duniya za ta bai wa Falasɗinu izinin kafa tutarta a cibiyar majalisar da ke a New York,a wani sabon mataki na fafutukar diplomasiyya da za ta kai ga amincewar majalisar da ƙasar a matsayin ƙasa mai cikakken yanci.

Nan gaba zuwa da yamma majalisar za ta gabatar da wani ƙudurin na musammun a kan lamarin a taron da za ta yi, wanda kuma bisa ga dukkan alamu ake ganin na cikka suna ne kawai.ko da shi ke ma kawo yanzu ana nuna rashin tabbas a kan matsayin ƙasashen Ƙungiyar Tarrayar Turai masu ra'ayoyi mabanbanta. Amirka da da Isra'ila na yin adawa da wannan ƙudiri kamar yadda suka yi a lokacin da Falasɗinu ta samu matsayin yar kallo a majalisar a shekarun 2012.