1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

EU: Karin wa'adin dokar takaita tafiye-tafiye

Binta Aliyu Zurmi
May 8, 2020

Kungiyar Tarayar Turai ta amince da tsawaita dokar takaita tafiye-tafiya a tsakanin kasashenta da kwanaki 30 duk da cewar hakan babban cikas ne ga cinikayya da yawon bude ido.

https://p.dw.com/p/3bxHj
Ylva Johansson | EU-Kommissarin für Inneres
Hoto: imago images/ZUMA Wire/F. Sierakowski

A tsakiyar watan Maris na bana ne kasashen 27 na kungiyar Tarayyar Turan suka amince da rufe iyakokinsu daga duk wasu harkoki na shige da fice da ba su da wani mahimmamci a yanzu a kokarin takaita yaduwar wannan annoba ta COVID-19 da duniya ke fama da ita.

Kwamishiniyar harkokin cikin gida a kungiyar Ylva Johansson, ta ce kungiyar ta EU za ta bude iyakokinta muddin al'amura suka sasauto, wanda dama dai babu wani shinge na shige da ficen a tsakanin kasashen kungiyar da ake kira Schengen.