1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

EU da Birtaniya na takun saka tsakaninsu

Mouhamadou Awal Balarabe
September 10, 2020

 Mataimakin shugaban hukumar zartaswa na EU Maros Sefcovic ya dibar wa Birtaniya kwanaki 20 domin ta janye kudirin dokar soke wani bangare na yarjejniyar Brexit, Sai dai Birtaniya ta yi kunnen uwar shegu da wa'adin.

https://p.dw.com/p/3iIlV
Maros Sefcovic
Hoto: picture-alliance/AP/F. Seco

Kungiyar Tarayyar Turai ta dibar wa Birtaniya har zuwa karshen wata Staumba don ta janye kudirinta na soke wani bangare na yarjejeniyar rabuwa da juna na Brexit idan tana son kanta da lafiya. Wannan wa'adin ya biyo bayan wani taro a Landan da EU ta kira cikin gaggawa da nufin samun karin haske kan aniyar Birtaniya na kin mutunta abin da suke cimma tun watanni taran da suka gabata.

Mataimakin Shugaban Hukumar zartaswa na EU Maros Sefcovic ya yi amfani da wannan dama wajen kira ga gwamnatin Birtaniya da ta janye kudirin dokar , Sannan ya jaddada cewa EU ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen klubalantar Birtaniya a kotun Turai ba. 
Sai dai a lokacin da yake maida martani, karamin ministan Birtaniya Michael Gove ya yi watsi da wa'adin na EU, inda ya ce gwamnatin Birtaniya  za ta ci gaba da bin kudirin na soke wasu tanade-tanade na yarjejeniyar ta Brexit.

  Wannan rikicin na faruwa ne a daidai lokacin da gwamnatin Birtaniyya ke ci gaba da zaman tattaunawa da EU kan dangantakar bangarorin biyu bayan raba gari kwata-kwata tsakaninsu.