1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Lafiya

Wani ya sake kamuwa da Ebola a Kwango

Gazali Abdou Tasawa
April 10, 2020

Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ko OMS ta sanar da sake gano wani mutun dauke da cutar Ebola a daidai loakcin da ya rage kwanaki uku a ayyana kawo karshen annobar cutar a kasar

https://p.dw.com/p/3alIj
Symbolbild Masernkrise
Hoto: picture-alliance/AP Photo/J. Delay

Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce an sake samun wani mutun dauke da cutar Ebola a Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango a wannan Juma'a a daidai lokacin da ya rage kwanaki uku Hukumar Lafiyar ta duniya ta ayyana kawo karshen annobar cutar ta Ebola a hakumance.

 Daraktan hukumar ta WHO ko OMS Tedros Adhanom Ghebreyesus ne ya sanar da wannan labari a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Tweeter a wannan Juma'a inda ya ce wannan na nufin assalatu ta warware a game da shirye-shiryen da ake na ayyana kawo karshen wannan Annoba ta Ebola a Jamhuriyar Dimukuradiyyar kwango.

 Ma'aikatar kiwon lafiya ta kasar Kwango Kinshasar ta bayyana cewa mutuman da aka sake samu da cutar ta Ebola wani matashi ne dan shekaru 26 mazaunin birnin Beni. Wannan dai shi ne mutun na farko da aka sake samu dauke da cutar ta Ebola a cikin kusan watanni biyu na baya bayan nan.