Duniya na da aiki a gaba a yaki da Ebola.
September 2, 2014Kungiyar likitoci ta Nagari na Kowa Medecins sans Frontieres ta kasa da kasa ta bayyana cewa bisa dukkan alamu duniya na neman gazawa a yaki da cutar Ebola kasancewar MDD ta yi gargadin cewa za a iya fiskantar karancin abinci a yankunan da wannan cuta tafi yin barna.
Kungiyar ta MSF ta fadawa MDD a birnin Newyork cewa shugabanni na kasashen duniya na gazawa a yakin da suke yi da wannan annoba, saboda haka sai suka bukaci shugabannin da su tasamma wannan annoba mai kudirin kare dangi na halittun dan Adam a duniya su aika da kayan agaji da maaikatan lafiya zuwa yammacin na Afrika.
Kungiyar likitocin ta ce a cibiyarta ta Laberiya da Saliyo mutane sun yi yawa hakan yasa mutane na mutuwa cikin iyalansu. A Saliyo wasu mutane da suka mutu ta sanadin kwayoyin cutar Ebola na mutuwa gawarsu na rubewa a tituna.
Kididdiga ta baya-bayannan da Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta fitar, ta nuna cewa mutane 1,552 suka mutu wasu kuma 3,062 suka harbu da kwayoyin cutar.
Mawallafi: Yusuf Bala
Edita :Usman Shehu Usman