Dubban 'yan Iraki na zanga-zanga a birnin Baghdad
April 27, 2016Talla
Kasar Iraki dai na fusakantar matsalolin siyasa, a yayin da Firiminisatan kasar Haider al-Abadi ke cigaba da kokarin kafa sabuwar majalisar zartarwar kasar da zata hado dukkanin bangarorin da basa ga miciji da juna.
Masu zanga-zangar dai na son ganin Shugaba Haider al-Abadi daukar kwararan matakan yin tankade da rairaya a cikin gwamnatin gami da kawo karshen cin hancin da rashawar da ya yiwa kasar katutu.
Bugu da kari a yayin da duban 'yan Irakin ke cigaba da zanga zangar, tuni 'yan majalisar dokokin Irakin suka amince da nada karin wasu da Shugaba Haider al-Abadin ya mika musu wadanda za a dana a mukaman ministocin kasar.