Chadi: Rasa rayuka bayan arangama tsakani makiyaya da manoma
August 28, 2019Rahotanni sun ce mutane 11 aka kashe a wani tashin hankali tsakanin makiyaya da manoma sakamakon wata takaddama dangane da lalata gonaki a kudancin kasar Chadi.
Gwamnan lardin Moyen-Chari Abbadi Sahir ya fada wa kamfanin dillancin labarun Faransa na AFP cewa rikicin ya barke ne a ranar Litinin a gundumar Koumogo, abin da ya janyo asarar rayukan makiyaya uku da manoma takwas.
Rikici tsakanin manoma da Larabawa makiyaya na zama babbar matsala a yankin Sahel mai fama da kamfar ruwa, inda ake yawaita samun tashe-tashen hankula kan mallakar filin noma ko na kiwo.
Wani basaraken yankin da ya ce a sakaya sunansa ya tabbatar wa kamfanin dillancin labarun na AFP yawan mutane da aka kashe, inda ya ce an kashe wani makiyayi ne bayan da shanunsa suka lalata shuki a wata gona. Su kuma makiyaya suka dauki fansa a kan manoman.