1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Burundi ta shirya ma zaben 'yan majalisa

Suleiman BabayoJune 28, 2015

Shugaban hukumar zaben Burundi ya ce suna shirye da gudanar da zaben 'yan majalisa kamar yadda aka tsara ranar Litinin, duk da tashin hankalin da ake samu

https://p.dw.com/p/1Foco
Straße in Bujumbura, Burundi
Hoto: Getty Images/AFP PHOTO/C.de Souza

Hukumar zaben kasar Burundi ta ce ta shirya wa zaben gobe Litinin, duk da tashe-tashen hankula da ake fuskanta masu nasaba da zaben. Mutane biyu sun hallaka a birnin Bujumbura fadar gwamnati kwana daya kafin zaben. Shugaban hukumar zaben ya ce tuni aka rarraba kayayyakin zabe a cikin mazabu fiye da 11,000 saboda zaben na 'yan majalisar dokokin.

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Ban Ki-moon ya na cikin wadanda suka nemi a jinkirta zaben, yayin da 'yan adawa suka janye, saboda shirin Shugaba Pierre Nkurunziza na sake takara domin neman wa'adi na uku. Fiye da mutane 70 suka hallaka cikin tashe-tashen hankulan na kasar ta Burundi, sannan manyan jami'ai na hukumar zabe, da fannin shari'a gami da mataimakin shugaban kasa na cikin dubban mutanen da suka arce daga kasar mai fuskuntar yiwuwar yakin basasa.