1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ghana: Bukatar ladaftar da minista

July 22, 2020

Gwamnati mai mulki da bangare masu rinjaye a majalisar dokokin Ghana, na kokarin kaucewa matsin lambar da gwamnati ke sha na cewa ta gurfanar da minista kana 'yar majalisaa gaban kwamitin ladabtarwa na majalisar dokokin.

https://p.dw.com/p/3fi6y
Afrika Ghana - Nana Akufo-Addo gewinnt Präsidentschaftswahl
Shugaban kasar Ghana Nana Akufo-Addo Hoto: picture-alliance/dpa/C. Thompson

Bukatar gurfanar da ministar kana 'yar majalisa da ke wakiltar jam'iyyar NPP a mazabar Ewutu Senya ta gabas a gaban kwamitin ladabtarwar na majalisar dokoki dai, ya biyo bayan harba bindiga sau hudu da ta yi a wani dandali da ake gudanar da atisayen rarraba katin zabe kana cikin cincirindon jama'a. Harbe-harben dai ya janyo an kame matasa hudu bisa zarginsu da aikata laifin harbi da kuma kona babura na ma'aikata, sai dai daga bisani ministar ta fito karara tana mai cewa: Babu wani mai makami a wajen, da kaina na harba bindigar domin gargadi, ko kuma ana so a nuna min cewar ba zan iya kare kaina ba ne?"

Majalisar wanzar da zaman lafiya ta Ghana tayi Allah wadai da wannan al'amari ta bakin shugabanta Rev. Emmanuel Asante. Duk da haka dai bangaren gwamnati da ke da rinjaye a majalisar dokokin kasar, ya wofintar tare da bayyana kiraye-kirayen da bukatar shugaban kasa ya tisge ministar ko kuma ta yi murabus da kanta, a matsayin wani abu da ba shi da tushe  balle makama.

Duk wani kokari na jin ta bakin gwamnatin da DW ta yi ya ci tura. Kwararru a kan harkokin tsaro sun nuna damuwarsu kan yadda rashin jure hamayyar siyasa daga jami'an gwamnati a Ghana ya kai kololuwa, musamman a yayin da zaben shugaban kasar ya rage kasa da watanni biyar. Abin jira a gani shi ne yadda doka za ta hukunta ko kuma kare ministar.