1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bincike kan harbin 'yan jarida a Afghanistan

April 4, 2014

Shugaba Hamid Karzai na Afghanistan ya nemi da ai bincike kan harbin da da aka yi wa wasu 'yan jarida biyu na kamfanin dillancin labarai na AP a kasar ta Afghanistan.

https://p.dw.com/p/1BcIQ
Afghanischer Präsident Hamid Karzai
Hoto: Johannes Eisele/AFP/Getty Images

Wata sanarwa da fadar gwamnatin kasar ta fidda a wannan Juma'ar ta ce Mr. Karzai ya damu matuka da harbin da wani baturen 'yan sanda ya yi wa 'yan jarida wanda hakan ya yi ajalin daya yayin da gudan ta samu mummunan rauni.

'Yan jiridar biyu wato Anja Niedringhaus 'yar kasar Jamus da Kathy Gannon da ta fito daga Canada sun gamu da wannan ibtila'i ne lokacin da dan sandan ya bude musu wuta sa'ada da suke zaune cikin motarsu a wani yanki da ke gabashin kasar.

Tuni dai kamfanin dillancin labaran na AP da gwamatocin kasashen da 'yan jaridar suka fito suka yi Allah wadai da harbin da aka yi, tare da neman gwamnatin karsar ta hukunta wanda ya aikata wannan danyen aiki.

Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Pinado Abdu-Waba