1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ban Ki-moon ya bukaci karin soje a Bangui

February 21, 2014

Majalisar Dinkin Duniya na kokarin aika karin dakaru dubu uku zuwa Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya domin kare fararan hulla daga cin zarafin da suke fuskanta.

https://p.dw.com/p/1BD8a
Hoto: Reuters

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Ban Ki-moon, ya bukaci Kwamitin Sulhu na Majalisar ya tura karin dakaru a kalla dubu uku da zasu hada da sojoji da 'yan sanda ya zuwa Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya cikin gaggawa domin sanya tsari tare da kariyar fararan hula a wannan kasa.

Ban Ki-moon ya kara da cewa wadannan dakaru za su isa Jamhuriyar Afirka ta Tsakiyar ba da jimawa ba, kuma tare da isassun kayan aiki musamman ma jiragyen zirga-zirga a cikin wannan kasa mai Fadin gaske.

A halin yanzu dai, dakarun kasar Faransa dubu biyu, da na kasashen Afirka dubu shida, sannan da na Tarayyar Turai a kalla dari biyar ke wannan kasa. Amma duk da haka ana ganin karin dakarun na Majalissar Dinkin Duniya, wani babban abun da ake jira ne.

Mawallafi: Salissou Boukari
Edita : Mouhamadou Awal Balarabe