1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

Myanmar : An hana lauyan Suu Kyi magana

Abdoulaye Mamane Amadou
October 15, 2021

Hukumomin mulkin soja a Bama, sun hana lauyan da ke kare hambararriyar shugabar kasar Aung San Suu Kyi ya sake tozali da 'yan jarida na ciki da wajen kasar har ma da ganawa ko tattaunawa da jakadun kasashen ketare.

https://p.dw.com/p/41iJP
Myanmar | Khin Maung Zaw Anwalt des inhaftierten Aung San Suu Kyi
Hoto: STR/AFP/Getty Images

Cikin wata sanarwa da ta fitar, gwamnatin mulkin sojan ta ce ta hana Khin Maung Zaw magana ne kasancewar kalamansa ka iya tayar da zaune tsaye a kasar. A wata ganawar karshe da 'yan jarida, lauyan ya gabatar musu da shaidar wani tsohon shugaban kasar da ya nada a gaban kotu, yana cewa sojojin da suka je kamashi da ya gwammace mutuwa maimakon ya yi marabus.

Tun bayan hambarar da ita daga kan karagar mulki sojoji a Myanmar ke zargin Aung San Suu Kyi da aikata manyan laifuka ciki har da na cin hanci, lamarin da ya janyo bore da ya yi sanadiyar mutuwar mutane dubu da 200 ba ya ga wasu fiye da dubu bakwai da ke hannun hukuma.