1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kokarin murkushe masu zanga-zanga a Burundi

Lateefa Mustapha Ja'afarMay 2, 2015

Gwamnatin kasar Burundi ta sha alwashin yin amfani da karfi wajen tarwatsa masu zanga-zangar adawa da shirin tazarce na Shugaban Pierre Nkurunziza.

https://p.dw.com/p/1FJ7C
Zanga-zangar adawa da tazarce a Burundi
Zanga-zangar adawa da tazarce a BurundiHoto: AFP/Getty Images/S. Maina

Gwamnatin dai na zargin 'yan adawa da kuma kungiyoyin fararen hula da suka shirya wannan zanga-zanga da yin hanya ga wadanda ta kira da 'yan ta'adda da suka kai wani hari kan jami'an 'yan sandan kasar da gurneti, harin da ya yi sanadiyyar mutuwar muitane uku ciki kuwa har da jami'an 'yan sandan biyu.

Ministan tsaron kasar Janar Gabriel Nizigama ya bayyana hakan inda ya zargi wadanda suka shirya zanga-zangar na da hannu a harin da aka kai din.