1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kamaru: Rikici ya barke a yankin Bamenda

Ramatu Garba Baba
April 25, 2019

Rahotannin na nuni da cewa, fada ya barke a tsakanin mayakan awaren yankin da ke magana da turancin Ingilishi da jami'an tsaro a garin Bamenda da ke Kamaru, lamarin da tuni ya haifar da rudani.

https://p.dw.com/p/3HSZZ
Kamerun Sprachenstreit um Englisch
Hoto: Getty Images/AFP

Barkewar rikicin na zuwa ne a daidai lokacin da Jan Egeland, wani jami'i na Kungiyar bayar da agaji ta kasar Norway, ya ke jan hankulan duniya kan su waiwayi bala'in da jama'ar da rikici ya daidaita a rikicin kasar na fiye da shekaru biyu ke ciki. Daruruwan mutane ne suka tserewa gidajensu inda suka zabi rayuwa cikin dazuka ba kuma tare da samun agaji daga ko ina ba kamar yadda aka saba gani a wasu kasashen duniya da ke fama da rigingimu.

A cewar Egeland jami'in na kasar Norway, da ya kai ziyara yankin da ke fama da tashe-tashen hankulan ya yi kira ga kungiyoyi na agaji da shugabannin kasashen Turai da su dubi halin da rayuwar wadannan mutane ke ciki su tallafa musu.