Angola: Shugaba Lourenco zai kama mulki | Labarai | DW | 15.09.2022
  1. Inhalt
  2. Navigation
  3. Weitere Inhalte
  4. Metanavigation
  5. Suche
  6. Choose from 30 Languages

Labarai

Angola: Shugaba Lourenco zai kama mulki

Za a rantsar da Shugaba Joao Lourenco na Angola a wa'adi na biyu a matsayin shugaban kasa, bayan da ya lashe zaben watan Agustan da ya gaba mai cike da takaddama.

Angola | Joao Lourenco | Shugaban Kasa | MPLA

Bayan lashe zabe, Joao Lourenco zai fara wa'adi na biyu na shugabancin Angola

Rahotanni sun nunar da cewa an tsaurarar matakan tsaro a dandalin Praca da Republica mai dimbin tarihi da ke Luanda babban birnin kasar ta Angola, inda za a rantsar da Shugaba Joao Lourenco na jam'iyyar MPLA mai mulki. Kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP ya ruwaito cewa, an hango jagororin babbar jam'iyar adawa daga nesa. Babbar jam'iyyar adawa a Angolan ta UNITA dai, ta yi korafin cewa an dauki matakin jibge dimbin sojoji a warin rantsar da sabon shugaban ksar ne domin a razana mutane. Ita dai jami'iyyar adawar ta UNITA ta sha kaye ne a hannun jam'iyyar MPLA mai mulki ta Shugaba Lourenco.