1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana zaben shugaban kasa a Mali

July 29, 2018

Shugaba Ibrahim Boubakar Keita na neman wani wa'adi na biyu na shekaru biyar a zaben da ake yi a wannan Lahadi.

https://p.dw.com/p/32G34
Wahlen in Mali 2013
Hoto: picture-alliance/AP

A wannan Lahadin ne al'umar kasar Mali ke gudanar da babban zabe, inda shugaba mai ci Ibrahim Boubakar Keita ke neman wani wa'adin na biyu na wasu shekaru biyar.

Mali dai na fama da matsalolin tsaro da suka hada da rikicin kabilanci da na masu tsattsauran ra'ayi, da ya kara muni cikin shekaru biyar na mulkin Shugaba Keitan.

'Yan takara 24 ne ke neman shugabancin kasar, a zaben da tuni wasu suka bayyana fargabar iya fuskantar turjiya daga 'yan bindiga.

Akwai dai manyan 'yan kasuwa da kuma wata mace guda da ke cikin jerin wadanda ke neman takarar.

'Yan kasar miliyan takwas ne aka yi wa rajista.

Za kuma a bude rumfunan zabe ne da misalin karfe takwas agogon kasar, a kuma rufe karfe shida na yammaci.