1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana tattara sakamakon zabe a Amirka

November 9, 2022

Bayan kammala zaben tsakiyar wa'adi a Amirka, ana ci gaba da harhada kan kuri'u daga yankunan kasar daban-daban. Da wuya dai a iya bayyana jam'iyyar da ta yi galaba yanzu.

https://p.dw.com/p/4JF2p
USA I Midterm 2022 I Gang zur Wahlurne
Hoto: Scott Olson/AFP/Getty Images

Ana can ana tattara sakamakon zaben tsakiyar wa'adi mai matukar muhimmanci da aka yi a fadin kasar Amirka a ranar Talata.

Sa'o'i gabanin rufe rumfunan zabe, alamu sun nuna cewa da wuya ne a iya bayyana jam'iyya daya tilo da ta samu rinjaye kai tsaye.

Sai dai hasashe na bayyana jam'iyyar Republicans ta tsohon shugaban kasar, Donald Trump a matsayin wacce ke iya samun rinjyen kujeru a majalisar wakilai, duk da cewa ba kai ga ganin samun rinjaye ba kawo yanzu.

A fili yake dai jam'iyyar Democrats ta Shugaba Joe Biden, na iya rasa iko a dukkanin majalisun Amirkar.

Kuma rashin karfin iko ko rinjaye a majalisun biyu, na nufin Shugaba Biden zai rika fuskantar tazgaro wajen iya cimma burin samun kafa dokoki da sauran bukatu a zaurukan duka biyu.