1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An zargi sojin Kamaru da kisan farar hula

Gazali Abdou Tasawa
March 28, 2019

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Human Right Watch ta zargi jami'an tsaron Kamaru da kisan fararan hula akalla 170 a watannin shida na baya bayan nan a yankin Anglophone na kasar Kamaru mai fama da rikicin 'yan aware. 

https://p.dw.com/p/3Fp94
Symbolbild zur Nachricht - Streitkräfte in Kamerun zerschlagen Boko-Haram-Schule
Hoto: Getty Images/Afp/Reinnier Kaze

A cikin wani rahoto da ta wallafa a wannan Alhamis, kungiyar ta HRW ta ce sojojin gwamnatin Kamarun sun yi amfani da karfin da ya wuce kima tare da kona daruruwan gidaje a yankin daga watan Oktoban bara ya zuwa yanzu. 

Sai dai rahoton ya ce ba sojojin kasar ta Kamaru ba ne ke da alhakin kisan illahirin mutanen 170, kana su kansu sojojin gwamnatin sun rasa mutane 31 a cikin fadace-fadace sama da 220 da suka wakana a yankin Arewa maso Yamma da Kudu maso Yamma na kasar ta Kamaru a tsukin watannin shida.

Sai dai kuma tuni gwamnatin kasar ta Kamaru ta yi watsi da wannan rahoto na kungiyar ta HRW ta na mai cewa ba shi da tushe balantana makama.