1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An tsananta tsaro a New Zealand

March 18, 2019

'Yan sanda a New Zealand sun bazu a sassan birnin Christchurch, yayin da harkoki ke budewa a makarantu da kasuwanni bayan harin ta'addanci na makon jiya.

https://p.dw.com/p/3FE1h
Neuseeland Terroranschlag auf Moscheen in Christchurch | Polizeipräsenz
Hoto: Reuters/E. Su

Wani mai suna Brenton Tarrant ne ya kai harin kan musulmi a masallatai biyu daban-daban inda ya halaka mutane 50 wasu kusan adadin ma suka jikkata.

Firaministar kasar, Jacinda Ardern, ta ce za a fidda sabbin dokoki kan mallakar bindiga cikin kwanaki goma.

Tuni kuwa aka garkame maharin yayin da ake ci gaba da bincike cikin wasu kasashen, kuma gwamnatin kasar na shirin wani zama na majalisar ministoci kan sabbin matakan tsaro.

Da ranar wannan Litinin ne ake sa ran gudanar da jana'izar wasu daga cikin wadanda lamarin na Juma'ar makon na jiya ya rutsa da su.