1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An sassauta dokar ta-bace a jihar Diffa

Lawan Boukar GAT
October 31, 2018

A jamhuriyar Nijar al'ummar jihar Diffa ta bayyana gamsuwarta da matakin da gwamnan jihar ya dauka na sassauta dokar ta bacen da gwamnati ta kaddamar a yankin da nufin yaki da Boko Haram.

https://p.dw.com/p/37Rt9
Niger Soldaten
Hoto: Getty Images/AFP/I. Sanogo

Matakin sassaucin ya tanadi bai wa jama'a damar gudanar da harakokinsu daga karfe biyar na safe zuwa karfe sha daya na dare.

Al'ummar jihar ta Diffa wacce ta jima tana korafi da wannan doka da ta ce ta kawo cikas ga rayuwar jama'a da harakokinsu na yau da kullum ta yaba da matakin sassauta dokar. Masu shaguna da tebura da masu sana'ar acaba da dai sauran harakokin kasuwanci sun bayyana jin dadinsu da yadda aka kara tsawaita wa'adin soma aikin dokar da dare inda a yanzu suke da damar ci gaba da harakokinsu kasuwancinsu har zuwa bakin magariba.

Nigeria Ausgabe von Nahrungsmitteln durch Hilfsorganisation
Hoto: Getty Images/AFP/I. Sanogo

Sai dai duk da haka wasu al'ummomin jihar ta Diffa sun bayyana bukatar kara yin sassauci ga dokar musamman dangane da abin da ya shafi amfani da ababen hawa a cikin dare ta yadda wadanda suka samu wata larura ko ta rashin lafiya ko kuma haihuwa a tsakiyar dare su iya amfani da mota domin zuwa assibiti.