1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An sanyawa kungiyar Houthi takunkumi

Ahmed SalisuApril 14, 2015

Majalisar Dinkin Duniya ta sanar da sanya takunkumi musamman ma na makamai kan kungiyar ta Houthi mabiya tafarkin shi'a da ke kasar Yemen wadda ke so karbe iko da kasar.

https://p.dw.com/p/1F8Wg
UN-Sicherheitsrat Abstimmung über Jemen
Hoto: REUTERS/L. Jackson

A dazu ne kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya amince da kakaba wannan takunkumi inda aka amince da shi da kuri'u 14, ko da dai Rasha ta yi rowar kuri'arta bisa dalilinta na son ganon takunkumin ya shafi bangarorin biyu da ke gaba da juna a kasar.

Wannan takunkumi dai zai shafi shugaban kungiyar Abdul-Malik al-Houthi da makarrabansa da suka hada da Abdullah Yahya al Hakim da Abd al-Khaliq al-Huthi da kuma tsohon shugaban kasar Ali Abdullah Saleh da dansa.