1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An sake ranar zabe a Kwango

December 20, 2018

Hukumar zabe mai zaman kanta ta Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango, ta dage zaben shugaban kasa da aka tsara yi a ranar Lahadin da ke tafe.

https://p.dw.com/p/3AScT
Demokratische Republik Kongo | Corneille Nangaa | Präsidentenwahl erst im Dezember 2018
Hoto: Getty Images/AFP/J. Wessel

Hukumar ta CENI wacce ta sanar da hakan da ranar yau, ta kai zaben ne zuwa ga ranar 30 ga watan nan na Disamba.

Hukumar ta fuskanci matsaloli ne a bangaren samar da takardun zabe, saboda a cewarta konewar da wadanda aka samu suka yi.

Wannan dai shi ne zaben da ake sa ran samun mika mulki daga wata gwamnatin zuwa wata a Kwangon mai fama da rigingimun siyasa. Shekaru biyu ke nan ana tsara zabe ana dagewa a kasar.

Tun da fari dai sai da babbar mai shigar da kara a Kotun hukunta manyan laifuka ta duniya, Fatou Bensouda, ta yi gargadi kan yiwuwar fuskantar manyan laifuka a zaben kasar Kwangon.