1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An sake kai hari a Kamaru

Abdourahamane HassaneJanuary 18, 2016

Rahotannin daga Kamaru na cewar an sake kai wani harin kunar baƙin wake a cikin wani masallaci a kauyen Nguetchewe da ke a yankin arewa mai nisan kan iyaka da Najeriya.

https://p.dw.com/p/1HfQ7
Kamerun/ Soldaten/ Boko Haram
Hoto: picture-alliance/dpa

Wata majiyar tsaro ta ce mutane huɗu suka mutu a nan take a lokacin da wani matashin da ke ɗauke da bam ya kutsa kai a cikin masallacin a lokacin da jama'a ke yin sallah asubahi.

Wannan shi ne karo na biyu ke nan da Ƙungiyar Boko Haram ke kai irin wannan hari a cikin masallaci a Kamaru.Bayan wanda ta kai a makon jiya a garin Kouyape da ke a arewacin ƙasar wanda a ciki mutane 12 suka rasa rayukansu.