An sake kai hari a Kamaru
January 18, 2016Talla
Wata majiyar tsaro ta ce mutane huɗu suka mutu a nan take a lokacin da wani matashin da ke ɗauke da bam ya kutsa kai a cikin masallacin a lokacin da jama'a ke yin sallah asubahi.
Wannan shi ne karo na biyu ke nan da Ƙungiyar Boko Haram ke kai irin wannan hari a cikin masallaci a Kamaru.Bayan wanda ta kai a makon jiya a garin Kouyape da ke a arewacin ƙasar wanda a ciki mutane 12 suka rasa rayukansu.