1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kawo karshen harin da 'yan Taliban suka kai

Mohammad Nasiru AwalJune 22, 2015

An kashe dukkan mutane bakwai da suka kai harin kan majalisar dokokin ta Afghanistan da ke birnin Kabul.

https://p.dw.com/p/1FlaM
Afghanistan Explosionen und Schüsse am Parlament in Kabul
Hoto: Reuters/A. Masood

An murkushe wani hari da mayakan kungiyar Taliban suka kai kan ginin majalisar dokokin Afghanistan da ke birnin Kabul. Kakakin ma'aikatar cikin gida ya ce an kashe dukkan mutane bakwan da suka kai harin. Da farko wani dan kunar bakin wake ya ta da bam a cikin wata mota kusa da ginin sannan dakarun tsaro sun kashe sauran abokan tafiyarsa. Akalla mutane 31 sun samu raunuka a harin. An kai harin ne lokacin bikin ransar da sabon ministan tsaro Mazum Staniksai. An ji karan harbe-harbe da tashin bama-bamai a kusa da ginin majalisar dokokin.