1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kai harin kunar bakin wake a Pakistan

Mouhamadou Awal Balarabe
April 26, 2022

'Yan kasar Chaina uku da ke aikin karantarwa a jami'a da direbansu dan Pakistan sun rigamu gidan gaskiya a wani harin kunar bakin wake da wata mace ta kai a Karachi da ke kudancin kasar.

https://p.dw.com/p/4ATOi
Pakistan Explosion Gelände einer Universität in Karachi
Hoto: Fareed Khan/dpa/AP/picture alliance

Kungiyar BLA da ke fafutukar 'yantar da Balochistan ta dauki alhakin harin da aka kai kan karamar bas kusa a jami'ar Karachi, inda ake koyar da harshe da al'adu da adabin Sinanci. 'Yan Chaina uku na daga cikin mutanen da suka mutu a wani harin kunar bakin wake

 Dama dai ayyukan da kasar Sin ke gudanarwa sun saba fuskantar kyama a Pakistan, musamman a tsakanin 'yan aware na Balochistan, wadanda suke zargin cewa ana mayar da su saniyar ware a yankin.

Sabon Firaministan Pakistan Shehbaz Sharif  ya yi amfani da shafinsa na Twitter wajen yin tir da abin da ya kira "aikin ta'addanci".

Tsaron ma'aikatan Chaina da ke aikin samar da ababen more rayuwa a Pakistan ya dade yana damun birnin Beijing, wadda ta zuba biliyoyin daloli a cikin 'yan shekarun nan