1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kai hari kan musulmi a New Zealand

March 15, 2019

Wani dan bindiga ya buda wuta kan masallata a birnin Christchurch na kasar New Zealand inda rahotanni ke cewa an tafka asarar rayuka.

https://p.dw.com/p/3F6M1
Neuseeland Schießerei in Moschee in Christchurch
Hoto: picture-alliance/AP Photo/M. Baker

Mutumin da aka ce ya kutsa masallacin al Nuri lokacin sallar Juma'a, sanye da bakaken kaya, ya buda wutar ne da wata bindiga mai sarrafa kanta, inda kuma ya kashe akalla mutum na akalla mutum 40.

Shaidu sun ce mutumin da ya kai harin ya sanya hular kwano da ke daukar naurar daukar hoton da ta watsa kai tsaye ta kafar sadarwar Intanet.

'Yan sanda sun gargadi jama'a da a guji yada hotunan harin ta shafukan sada zumunta, saboda muninsu. Galibin wadanda ke masallacin dai baki ne da suka fito daga wasu kasashe.

Firaministar New Zealand, Jacinda Ardern, ta bayyana harin da cewa na ta'addanci ne.

Ana kuma tsare da mutane hudu da suka hada da wani dan kasar Ostireliya da  kuma wata mace guda.