1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kasa cimma yarjejeniyar mulki a Sudan

Abdul-raheem Hassan
May 21, 2019

Shugabannin majalisar soji da bangaren masu zanga-zanga sun kasa kulla yarjejeniyar kafa sabon kwamitin shugabancin rikon kwarya saboda rashin amincewa da bangaren da zai yi jagoranci.

https://p.dw.com/p/3Io9D
Sudan Khartum Proteste gegen Militär-Regierung
Hoto: AFP/M. El-Shahed

Sojojin kasar Sudan da suka jagoranci kifar da gwamnatin tsohon Shugaba Omar al-Bashir na fuskantar matsin lamba daga kasashen waje kan mika mulki ga farar hula, abinda ke zama babban burin masu zanga-zangar.

Bangarorin biyu sun sha shiga tattaunawa don kafa sabon kwamiti da zai ja ragamar mulkin kasar na tsawon shekaru uku kafin gudanar da zabe, kungiyoyin farar hula na fatan samun rinjaye a cikin mabobin kwamitin mulkin. Ana sa rai bangarorin biyu za su sake komawa teburin tattaunawa domin samun mafita kan rikicin da kasar ke ciki.