1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An bude tashoshin zabe a Baharain

Yusuf Bala Nayaya MNA
November 24, 2018

Al'ummar kasar Baharain sun fita kada kuri'a a zaben 'yan majalisar kasar duk da kiraye-kirayen su kaurace wa zaben da jam'iyyun siyasa na adawa da aka rushe ba sa cikinsa.

https://p.dw.com/p/38q6A
Wahlkampf in Bahrain
Hoto: AFP/Getty Images

Manyan jam'iyyun adawa biyu Al-Wefaq ta 'yan Shi'a da Waad masu nesanta kai da addini an haramta masu shiga wannan zabe dalilin da ya jawo sabon kira na a kauce wa zaben 'yan majalisar a Baharain.

Sarki Hamad a watan Satumba ya nemi al'umma su fita zaben wanda jami'ai ke cewa akwai mutane 293 ciki har da mata 41 wadanda ke neman kujerun majalisa a kasar ta Baharain.

Da misalin karfe takwas agogon Baharain wato biyar agogon GMT aka bude tashoshin kada kuri'a yayin da za a rufe da karfe takwas na yamma.