1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amirka: An janye haramci shiga ga 'yan Chadi

Yusuf Bala Nayaya
April 11, 2018

Kasar da ke a Tsakiyar Afirka ta inganta harkoki na tsaronta ta kuma kara yawan musayar bayanai da take yi da Amirka.

https://p.dw.com/p/2vpIW
Präsident Tschad - Idriss Déby Itno
Hoto: UImago/Xinhua/C. Yichen

Shugaba Donald Trump a ranar Talata ya janye sanya takunkumi na hana al'ummar kasar Chadi ziyartar kasar Amirka abin da ke zuwa bayan watanni ana nazarin kasar.

Kamar yadda fadar White House ta bayyana kasar da ke a Tsakiyar Afirka ta inganta harkoki na tsaronta, ta kuma kara yawan musayar bayanai da take yi da Amirka kan abin da ya shafi al'ummarta.

Kasar ta Chadi dai ta kasance cikin kasashe takwas da Amirka ta sanya masu takunkumi na hana shigar al'ummarsu kasarta, kasashen da suka hadar da Iran da Libiya da Siriya da Somaliya da Yemen da Banizuwela da Koriya ta Arewa. Kasar ta Chadi dai ana kallonta a matsayin muhimmiyar kasa ga Amirka a fagen yakin da take yi da ta'addanci.