1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jama'a na neman Abdelaziz Bouteflika ya sauka daga mulki

Abdourahamane Hassane
February 25, 2019

A Aljeriya darurruwan jama'a sun gudanar da zanga-zanga a birnin Alger domin nuna adawa da takarar Abdelaziz Bouteflika a wa'adi na biyar a zaben shugaban kasar da za a yi nan gaba a cikin wannan shekara.

https://p.dw.com/p/3E3kG
Algerien Demonstration Ausschreitungen
Hoto: picture-alliance/dpa

Masu zanga-zangar wdanda tun suna karamin gungun jama'a har suka kai darurruwa sun ci gaba da yin zanga-zangar duk da yunkurin da 'yan sanda suka yi na tarwatsu da borkonon tsohuwa. Hadin gwiwar kungiyoyin farar hula wadanda  ake kira Mouwatana wadanda aka girka a shekar bara domin nuna adawa da takarar ta biyar ta  Abdelaziz Bouteflika su ne suka kira gangamin.