1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Binciken baraguzai bayan girgizar kasa

October 31, 2020

Masu aikin ceto na cigaba da binciken baraguzan gine gine bayan girgizar kasar da ta auku a Girka da Turkiya ko za a sami gano wasu mutanen da suka tsira da rayukansu.

https://p.dw.com/p/3kgWH
Türkei Izmir | Erdbeben
Hoto: Depo Photos/abaca/picture alliance

Girgizar kasar wadda ta auku a jiya Juma'a ta yi sanadiyar mutuwar mutane 26 wasu da dama kuma suka jikkata. Girgizar kasar mai karfin maki bakwai a ma'aunin Richter ta haifar da tashin igiyar ruwan tsunami a yankin tsibirin Samos wanda ya janyo ambaliyar ruwa a gabar kogi a yammacin Turkiyya.

An jiwo amon girgizar kasar a cikin birnin Istanbul da kuma Athens. Girgizar kasar dai ta bude kofar tattaunawa ta diflomasiyya a tsakanin kasashen biyu da ke takun saka a kwanakin nan.

Tuni Firaministan Girka ya kira shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ta wayar tarho domin yi masa jaje da kuma ta'aziyya.