Aikin ceto a Makkah bayan rushewar wani otel
January 6, 2006Talla
Masu aikin ceto a Saudiya na ci-gaba da aiki don ceto wadanda watakila ke da sauran numfashi a karkashin wani otel da ya rushe jiya a birnin Makkah. Ya zuwa yanzu an tabbatar da mutuwar mutane 20 yayin da 59 suka samu raunuka sakamakon ruftawar otel din dake kusa da Kabah a daidai lokacin da ake dab da gudanar da aikin hajji na bana. Daga cikin wadanda wannan hadari ya rutsa da su akwai ´yan kasar Masar, Tunisia da Hadaddiyar Daular Labarawa sai kuma ´yan kasar Indonesia. A bana ana sa rai mutane miliyan 2.5 zasu yi aikin hajji a kasa mai tsarki.