AFCON: Senegal za ta fuskanci Maroko a wasan karshe
January 15, 2026
Talla
Senegal da mai masauki Morocco sun tsallake zuwa wasan karshe na gasar cin kofin Afirka (AFCON), bayan da suka yi nasara a wasanninsu na zagayen dab da na karshe a daren jiya.
Zakunan Teranga na Senegal sun doke Masar da ci daya da nema, inda Sadio Mané ya zura kwallo daya tilo a minti na 78.
A daya wasan kuma, Najeriya ta fice bayan da Morocco mai masauki ta doke ta a bugun fenarati da ci 4–2, bayan kammala cikakken lokaci na wasan da ma karin mintuna 30 babu wanda ya zura kwallo.
A ranar Asabar, Masar da Najeriya za su kara a birnin Casablanca domin neman matsayi na uku.
Sai kuma ranar Lahadi, Senegal da Morocco za su fafata a wasan karshe a birnin Rabat domin sanin wadda za ta lashe kofin na bana.