1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zanga-zangar adawa da wariyar launin fata na karuwa

Ramatu Garba Baba
June 3, 2020

Faransa da Britaniyya na daga cikin kasashen duniya da aka samu dubban masu zanga-zangar adawa da wariyar launin fata makamancin wanda ke gudana a Amirka bayan kisan George Floyd.

https://p.dw.com/p/3dCDI
Frankreich Demonstration in Paris in Erinnerung an Adama Traore
Hoto: Reuters/G. Fuentes

A yayin da zanga-zanga ke ci gaba a wasu jihohin Amirka bayan kisan wani bakar fata George Floyd da wani Dan sanda farar fata yayi, wasu gwamnatocin kasashen duniya son soki matakin da gwamnatin Shugaba Donald Trump ta dauka a kokarin shawo kan rikicin.

Chaina da ta sha suka da matakan ladabtarwa daga Amirkan ta hanyar aza mata takunkumi bisa zargin tauye hakkin dan adam, na daga cikin kasashen da suka soki matakin amfani da karfin da ya wuce kima kan masu zanga-zanga adawa da wariyar launin fata, kasar Iran da ita ma ta dandan kudarta a hannun Amirka,  a nata bangaren ta yi tsokaci, inda ta yi amfani da ire-iren kalaman Shugaba Trump ga al'ummar Iran a yayin duk wata zanga-zanga na cewa duniya ta ji kukansu kuma tana tare dasu.

Afrika ta Kudu ita ma ta shawarci gwamnatin Amurka da ta sassauta matakan da ta ke dauka kan masu boren, hakazalika Firaiministan Britaniyya Boris Johnson da Shugaban darikar Katolika Fafaroma Francis.Yanzu haka akwai kasashen duniya da jama'a ke gudanar da zanga-zangar lumana don adawa da wariyar launin fata.