1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zaman lafiya tsakanin Falasdinu da Isra'ila

July 18, 2013

Shugabannin Falasdinu za su jefa ku'riar tantance komawa ga zaman sulhu da Isra'ila, ba tare da sharadi ba.

https://p.dw.com/p/19AJW
Mahmud Abbas (R), head of the PLO team, and Israeli Foreign Minster Shimon Peres hold a joint press conference at Cairo's Presidential Palace 29 December 1993. Peres said that the two delegations had reached an understanding on how to lift obstacles which have delayed the start of Palestinian self-rule but fell short of a breakthrough agreement. (Photo credit should read STR/AFP/Getty Images)
Hoto: STR/AFP/Getty Images

Wani jami'in hukumar Falasdinu ya sanar da cewar a wannan Alhamis (18. 07. 13) ce jagororin Falasdinu za su jefa kuri'a a kan daftarin shirin samar da zaman lafiya tare da Isra'ila, wanda kasar Amirka ta tsara, amma kuma ba tare da gindaya sharadin da ya shafi batun yankunan da ita Isra'ilar ke ci gaba da mamaya ba. Jami'in ya ce abin da ya fi muhimmanci dangane da daftarin da sakataren kula da harkokin wajen Amirka John Kerry ya tsara, shi ne sake komawa ga tattaunawar, amma ba tare da dakatar wa ko kuma hana ci gaba da samar da matsugunai a yankunan Yahudawa'yan kama-wuri-zauna ba. Ya kara da cewar, daftarin na Kerry, ya kuma tanadi cewar, idan har Isra'ila ta ci gaba da gina sabbin matsugunai a dai dai lokacin da tattaunawar ke ci gaba da gudana, to, kuwa, su ma Falasdinawa za su iya sake gabatar da bukatarsu ta shiga cikin kungiyoyin kasa da kasa, inda kuma za su nemi daukar matakin shari'a a kan gwamnatin isra'ilar.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Umaru Aliyu