1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaTurai

Shugabanin kasashen duniya na taya Joe Biden murna

Umar Zahradeen RGB
November 9, 2020

Shugabannin kasashen duniya na cigaba da mika sakoninsu na murna ga Joe Biden bayan nasarar da ya samu a zaben shugaban kasa na Amirka da aka yi a makon jiya.

https://p.dw.com/p/3l3PR
USA Wilmington | Rede Joe Biden und Kamala Harris nach dem Wahlsieg
Hoto: Angela Weiss/AFP/Getty Images

Zababben Shugaban Amirka Joe Biden na ci gaba da karbar sakonnin taya murna daga ciki da wajen nahiyar Amirka. Daga bangaren kudu da arewa gabas da yamma ko ina ka juya a wannan duniya, jama'a na mayar da martani, galibi ana murnar lashe zaben wanda Shugaba Trump ke ci gaba da kartar kasa kan sakamakonsa. Kungiyar Tarayyar Turai ta EU na cikin wadanda suka ce a shirye suke su yi aiki tare da zababben Shugaba Joe Biden.

 Zababben Shugaban Amirka Joe Biden da mataimakiyarsa  Kamala Harris
Zababben Shugaban Amirka Joe Biden da mataimakiyarsa Kamala Harris Hoto: Andrew Harnik/Getty Images

Aika sakonnin murna daga sassan duniya

Shugabar hukumar gudanarwa ta kungiyar Ursula von der Leyen ta bayar da tabbaci tana mai cewa..''Ina son tabbatar muku da cewa Kungiyar EU a shirye take ta kara fadada hadin gwiwarta da sabon shugabancin na Amirka. Akwai gagarumin aiki a gabanmu amma za mu iya dorawa daga dangantarkar da muke da ita da su a halin yanzu.''To sai dai ga Firaminsitan Birtaniya Boris Johnson batun kasuwanci da sauyin yanayi, su ne zai so zababben shugaban na Amirka ya mayar da hankalinsa a kai..''Ina fatan yin aiki kafa da kafa da shi, kan abubuwa masu muhimamnci a nan gaba kadan. Ina son mu duba batun magance sauyin yanayi da kasuwanci da kuma samar da tsaro a kasashen duniya.''

Frankreich Straßurg Europatag Flaggen Europaparlament Gebäude
Kasashen Turai sun baiyana anniyar aiki tare da Joe BidenHoto: picture-alliance/dpa/Mandoga Media

Bude sabon babi tare da Joe Biden

Birtaniyar da Jamus da Faransa  na cikin sahun farko na kasashen da  suka taya zababben shugaban Amirkan murna, inda tun ma a karshen mako Ministan Harkokin Wajen Jamus Heiko Maás ya soki tirjiyar da Shugaba Trump ke yi kan sakamakon zaben, inda Maas ya ce mutanen da suka fadi zabe kuma suka rungumi kaddara sun fi mutanen da suka yi nasara a zabe taimaka wa dimukuradiyya. Wasu 'yan kasashen China da Iran da Japan da DW ta tattauna da su, dukkansu na ganin cewa Shugaban Amrka mai barin gado Donald Trump bai riki dangantar da ke a tsakanin Amirka da kasashensu da hannu biyu ba. Sai dai masu sharhi na cewa ga irin wadanann kasashe, Joe Biden ka iya bude musu sabon babi.