1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Za je zagaye na biyu a zeɓen Mali

November 28, 2013

Sakamakon wucin gadi na zaɓen 'yan majalisun dokokin da hukumar zaɓen ta bayyana na nuna cewar babu wata daga cikin jam'iyyun siyasar da ta samu rinjaye a zagayen farko.

https://p.dw.com/p/1AQ2f
epa03964434 A picture made available 25 November 2013 shows Malian women trying to find their names on voting lists at a polling station in the Badalabougou neighborhood of Bamako, Mali, 24 November 2013. Malians voted for legislative elections amidst concerns over security following attacks in the northern city of Gao and the kidnapping and killing of two French journalists in the desert city of Kidal earlier this month. Some 1,080 candidates, including 135 women, are competing for 147 seats in the elections, which will go to a second round on 15 December unless one party wins an absolute majority. There are some 6.5 million eligible voters in the West African nation. EPA/TANYA BINDRA +++(c) dpa - Bildfunk+++
Hoto: picture-alliance/dpa

Hukumar ta ce ya zama dole a gudanar da zagaye na biyu na zaɓen 'yan majalisun dokokin ranar 15 ga watan Disamba da ke tafe. Daga cikin kujeru 147 da aka ware a majalisar dokokin, kujeru 16 kawai jam'iyyun siyasar da suka yi takara suka samu.

Wadanda suka haɗa da jam'iyyar shugaban ƙasar Ibrahim Boubacar Keita wato RPM wacce ta sami kujeru guda takwas,da jam'iyyar Soumaila Cisse ta URD da ta samu kujeru biyar yayin da ADEMA ta ke da kujeru guda biyu.Hukumomin ƙasar ta Mali dai sun ce jama'a ba su fito ba a zaɓen.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Umaru Aliyu