1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Assange na fuskantar tuhume-tuhume 18

January 4, 2021

Hukumomin Amirka sun sha alwashi maido shari'ar mai shafukan WikiLeaks a kasar.

https://p.dw.com/p/3nVTf
London Anhänger von Assange jubeln
Hoto: Henry Nicholls/REUTERS

Wata kotu a Birtaniya ta yi watsi da bukatar Amirka, dangane da batun mika mata mutumin nan da ke bankado bayanan sirri tare da wallafa su a shafukan intanet na WikiLeaks. Sai dai Amirkar ta ce ba za ta yi kasa a guiwa ba wajen ganin an hanna ta mutumin dan asalin kasar Ostireliyakuma a cewar hukumomin kasar ta Amirkar masu shigar da kararta sun shirya tsaf domin kalubalantar hukuncin kotun da ke birnin Landan.

Julian Assange mai shekaru 49 da haihuwa na fuskantar tuhume-tume 18, cikin su har'da na bankado bayanan sirrin hukumar sojojin Amirkar.