1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zaɓe a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya

Abdourahamane HassaneFebruary 14, 2016

'Yan takara biyu ne watau Anicet George Dologuele da Faustin Archange Touadera ke fafatwa a zagaye na biyu na zaɓen shugaban ƙasa da na 'yan majalisun dokoki.

https://p.dw.com/p/1Hv8d
Zentralafrikanische Republik Bangui Wahlen Wahllokal
Hoto: picture-alliance/AP Photo/H. Diaspora

A zagaye na farko na zaɓen shugaban ƙasar da aka yi Anicet Dologuele shi ne ke kan gaba da kishi 24 cikin 100 na ƙuri'un da aka kaɗa yayin da Faustin Touadera ke da kishi 19 da 'yan kai cikin 100.
Ƙasar ta jamhuriyar Afirka ta Tsakiya ta faɗa cikin wani tashin hankali na rikicin addini tsakanin musulmi da kirista a shekarar 2013, bayan da ƙungiyar Seleka ta musulmi ta ƙwaci iko daga hannu François Bozizé, abin da ya janyo asarar rayukan jama'a da dama.